Daukar Fansa: Mai tsaron lafiyar minista ya harbe ministan har lahira saboda rashin biyanshi albashi

Charles Engola, karamin ministan Kwadago, aiki da huldar masana’antu na Uganda, mai tsaron lafiyarsa ya harbe shi har lahira.
Fred Enanga, kakakin ‘yan sanda, ya ce an harbe ministan ne da misalin karfe 8 na safe agogon kasar ranar Talata a gidansa da ke Kampala, babban birnin kasar.
Enanga ya ce lamarin kisan kai ne.
“Daya daga cikin masu tsaronsa ne ya harbe shi (Engola) a gidansa da ke Kyanja wanda ake zargin ya yi harbi da yawa a kusa da wajen. Ya gudu daga wurin har zuwa cibiyar kasuwanci da ke Kyanja, Ring road inda ya shiga wani salon kuma ya harbe kansa har lahira,” in ji kakakin ‘yan sandan.
An bayyana wanda ya harbi Wilson Sabiiti, tsohon soja.
Wani ganau ya ce Sabiiti ya koka da cewa bin bashin albashi na watanni da dama da ba a biya ba yayin da yayi harbi a iska don gargadin farar hula a garin Kyanja, ‘yan mintuna kadan kafin ya juya kanshi da bindiga.
“Mai gadin ya ce ba a biya shi Ush4 miliyan (kimanin dala 1,000 ba). Ya ce yana da mace mai juna biyu kuma ‘ya’yansa ba sa zuwa makaranta, amma duk da haka ‘ya’yan ministar suna makaranta,” inji ganau din.
‘Yan sanda sun ce an fara bincike tare da nuna bakin cikin lamarin.
“Har yanzu ba a tabbatar da dalilin kisan ba. A halin yanzu binciken yana kan matakin farko na bita, tare da CID da ƙwararru, sun riga sun tattara bayanan wurin,” in ji Enanga.
“DiGP da tawagar daraktoci sun ziyarci wurin da lamarin ya faru tare da mika sakon ta’aziyya ga ‘yan uwa da abokan arziki.
“Muna so mu kara mika sakon ta’aziyya ga H.E. Shugaban kasa, dukkan ministocin gwamnati, ma’aikatan ma’aikatar kwadago, jinsi da ci gaban zamantakewa.

