Ilimi
Shirin Ciyar Da Dalibai A Lokacin Zaman Gida Ya Lakume Sama Da N500m, Inji Minista Sadiya Umar.

Gwamnatin Tarayya ta kashe kusan miliyan N523.3 a shirin ciyar da ‘yan makaranta yayin kulle-kullen cutar Covi-19.
Ministan Harkokin agaji, Gudanar da Bala’i da Ci gaban Al’umma Sadiya Farouq ce ta sanar da hakan a taron tattaunawa na shugaban kasa kan COVID-19 ranar Litinin a Abuja.