Jami’ar Sufuri Ta Daura Zata Lakume N18bn, Zata Kasance A Watan Satumba 2021 – Amaechi.
Ministan sufuri, Mista Rotimi Amaechi, ya ce $ 50 miliyan (kimanin N18bn) Jami’ar sufuri ta Daura, Jihar Katsina za ta lakume a watan Satumba, 2021.
Ya bayyana hakan ne a ranar Asabar din da ta gabata yayin gudanar da binciken cibiyar a Daura.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi bikin din jami’ar a watan Disamba na 2019 amma cutar COVID-19 ta dakatar da aikin.
Ya sake nanata cewa Jami’ar wani nauyi ne na zamantakewar CCECC, kamfanin da ke tafiyar da dukkan ayyukan layin dogo a Najeriya a halin yanzu.
Ministan ya ce “akwai hayaniya da yawa game da CCECC ba ta fara gina Jami’ar sufuri ba amma suna yin gine-gine,” in ji ministan.
“Sun samu yardar ne daga gwamnatin jihar kuma ingantaccen aikin gini ya fara a karshen Satumba.

