Labarai

Ka Yi Hankali Da Masu Zanga-zangar ENDSARS, Ina Ga Akwi Boyayyar Manufa Aciki – Shugaban APC Ya Gargadi Buhari.

Shugaban kwamitin riko na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Gwamna Mai Mala Buni na jihar Yobe ya gargadi gwamnatin Buhari da tayi taka tsan-tsan game da zanga-zangar da ke faruwa a duk fadin kasarnan.

Gwamnan ya ce akwai yiwuwar wata boyayyiyar manufa a bayan zanga-zangar adawa da ‘yan sanda masu yaki da fashi da makami (SARS) a duk fadin kasarnan.

Buni wanda yake magana a wata hira da sashen Hausa na BBC, ya ce akwai bukatar gaggawa ga shugabanni a dukkan matakai su hadu don kawo karshen zanga-zangar kafin ta yi waje.

“Idan aka kalli zanga-zangar a yanzu, sai kace wani abu mara kyau ya buya.

Duk da matakan da gwamnati ta dauka kan bukatun masu zanga-zangar, har yanzu suna kan tituna suna zanga-zangar.

Dole ne gwamnati tayi taka tsan-tsan da su.

“Me kuma masu zanga-zangar suke so?

IG ya dauki matakin gaggawa. Don haka, ina ganin ya kamata su dakatar da zanga-zangar su hau teburin tattaunawa da gwamnati don a samu mafita, ”inji shi.

Ya ce Shugaba Muhammadu Buhari ya karbi mulki a daidai lokacin da kasar ke fuskantar babban kalubale, yana mai jaddada cewa ba za a iya daidaita Najeriya a cikin shekaru biyar ba.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button