Labarai

Mutum 69 Ne Suka Mutu Yayin Zanga Zangar EndSars, Cewar Shugaban Kasa

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce an kashe mutum 69 a zanga-zangar adawa da cin zarafin ‘yan sanda da aka shafe tsawon kwanaki ana yi a kasar.

Ya ce wadanda suka mutun sun hada da farar hula, da jami’an ‘yan sanda da sojoji.

Ita dai kungiyar kare hakkin dan adam ta Amnesty International ta ce a ƙalla mutane 56 ne suka mutu tun fara zanga-zangar, ciki har da masu zanga-zanga 12 da aka kashe a Legas ranar Talata.

Wani rukuni da ya zama jigon shirya zanga-zangar yanzu ya nemi mutane su zauna a gida.

Kungiyar Feminist Coalition mai fafutukar kare hakkin mata, ta shawarci mutane da su bi duk wata dokar hana fita da ka aka sanya a jihohinsu.

Titunan babban birin Najeriya, da Lagos, da cibiyar zanga-zangar, sun yi tsit amma har yanzu akwai sauran fargaba.

Daga Comr Haidar Hasheem Kano

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button