Tinubu ya nada Nyesom Wike, Nasir El-Rufai, David Umahi, da wasu 25 a matsayin ministoci


Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ya sanar da sabbin sunayen ministocin a zauren majalisar a ranar Alhamis
A ranar Alhamis ne majalisar dattawa ta sanar da nadin ministocin da shugaba Bola Tinubu ya yi.
Wadanda ke cikin jerin sunayen, kamar yadda shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya bayyana a zaman taron na ranar Alhamis, sun hada da Abubakar Momoh, Yusuf Maitama Tukar, Ahmad Dangiwa, Anachu Muzawa, Uche Nnaji, Betta Edu, Doris Aneth Uzoka, David Umahi.
Sauran sun hada da: Nyesom Wike, Muhammad Badaru, Nasir El-Rufai, Nkiru Oyejiocha, Olubumbi Tunji Ojo, Stella Okotete, Uju Kennedy Ohaneye da Bello Muhammad Goroyo.
Sauran sun hada da Dele Alake, Lateef Fagbemi, Mohammad Idris, Olawale Edun, Waheed Adebayo Adelabu, Suleiman Ibrahim, Ali Patteh, Abubakar Kyari, John Eroh, Sani Abubakar Danladi, Ekperipe Ekpo da Farfesa Joseph.
Ana sa ran mika cikakken jerin sunayen, wanda dole ne ya kunshi akalla mutane 36 don cika sharuddan tsarin mulki, kafin a kammala tantancewa.
Jerin sunayen na zuwa ne a rana ta karshe da ya kamata Mista Tinubu ya mika sunayen ministocinsa ko kuma ya yi kasadar sabawa sabon gyara ga kundin tsarin mulkin Najeriya, wanda ya bai wa shugaban kasar kwanaki 60 ya kafa majalisar ministoci bayan rantsar da shi.

